طاهر جبريل دكو
_23 _February _2015هـ الموافق 23-02-2015م, 12:36 AM
DAGA INA SAHU YAKE FARAWA ?
Tambaya :
Assalamu alaikum mal ya gida ya kuma aiki, mal don Allah innada tambaya mal sahun sallah kan ta dama za'a fara ne ko ta hagu.?
Amsa :
To dan'uwa sahun da yake bin liman zai fara ne daga bayan liman ma'ana a sanya liman a tsakiya, saboda fadin Annabi s.a.w. "Masu hankali daga cikinku, su bi bayana" kamar yadda Muslim ya rawaito a hadisi mai lamba ta : 116. sannan da fadin Anas RA lokacin da yake bada labarin ziyarar da Annabi s.a.w. ya kai gidansu : " Sai muka tsaya ni da marayan a bayansa" kamar yadda Bukhari ya rawaito a hadisi mai lamba ta :694, daga nan kuma sai a cigaba da cika shi ta bangaren dama.
Haka nan ake so sahu na biyu shi ma ya kasance, ya fara daga tsakiya ya tafi zuwa dama, saboda fadin Bara'u dan Azib RA "Mun kasance idan muka yi sahu a bayan Annabi s.a.w. mu kan so mu kasance a damansa, ya fuskanto mu da fuskarsa " Muslim a hadisi mai lamba ta : 709.
Allah ne mafi sani
Jamilu Zarewa
21\2\2015
TA YI ALWALA DA RUWAN FITSARI, HAR TA YI SALLAH BA TA SANI BA
TAMBAYA:
Nakasan ce lokacin da Ina bording school idan senior na ya aikeni debo ruwa kafin na kawo masa ruwan sai nayi fitsari acikin rowan, kuma ban san adadin mutanen dana yiwa hakan ba, saboda ganin yadda senior yin mu suke gallaza mana da sunan seniority ga shi yanzu ban san inda zan gansu ba ballantana na nemi afuwar su, me ya kamata na yi kenan a yanzun? nagode, Allah ya kara maka imani da ilmi mai amfani
Amsa :
To 'yar'uwa ina rokon Allah ya kare mu daga irin wannan danyan aikin, Allah ya sa su kuma shawagabannin makarantu su kula da irin wannan cin zalin, ina baki shawara ki yawaita istigfari, mutukar lokacin da kika yi hakan kin balaga, su kam sallarsu da wankansu sun inganta, saboda a zance mafi inganci na malamai duk wanda ya yi alwala da ruwa mai najasa, bai kuma gano hakan ba, sai bayan lokacin sallar ya fita, to ba zai sake sallar ba, haka ma wanda ya yi wankan janaba, saboda addinin musulunci addini ne mai sauki.
Allah ne mafi sani
.
Duba Al'ausad na Ibnul- munzir shafi na 18 .
Jamilu zarewa
14\2\2015
ZAMAN GULMAR SHUWAGABANNI DA 'YAN SIYASA
Tambaya :
Assalãmu Alaykum, Yaa Shaykh, menene hukuncin magana akan shugabanni da 'yan siyasa? Shi ma gulma ne ko akwai banbanci idan mutumin yana da nauyin yiwa al'umma shugabanci da hidima? Jazakumullahu Khayran
Amsa :
To dan'uwa Allah da manzonsa sun haramta cin naman mutane, sannan malamai suna cewa : gulmar shuwagabanni da malamai ta fi tsananin haramci , saboda cin naman shuwagabanni zai jawo ayi musu tarzoma, kamar yadda cin naman malami zai jawo a raina ilimi, saidai akwai wuraren da ya halatta a ci naman mutane saboda maslaha, kamar idan aka zalunci mutum to ya halatta idan zai kai kara ya bayyana zaluncin da aka yi masa, haka nan idan ya ga wani sharri yana so a taimaka masa wajan gusar da shi to ya halatta ya fadi sunan mai laifin, kamar yadda kuma ya hallata ayi gulmar mutumin da ya shahara da aikata sabo da fasikanci, don a guji sharrinsa. Duba Azkar : 489 da kuma Majmu'ul fataawa 28\221 .
A bisa abin da ya gabata za mu fahimci cewa : duk kasar da ake kafa shugaba ta hanyar zabe, to ya hallata mutane su tattauna matsalolin shugaban da yake kai, domin tunanin kawo canji a zabe mai zuwa, musamman idan shugaban ya kasance azzalumi kuma fasiki mai yawan aikata sabo, saidai ya wajaba maganar ta su ta zama gwargwadon bukata.
Allah ne mafi sani.
Tambaya :
Assalamu alaikum mal ya gida ya kuma aiki, mal don Allah innada tambaya mal sahun sallah kan ta dama za'a fara ne ko ta hagu.?
Amsa :
To dan'uwa sahun da yake bin liman zai fara ne daga bayan liman ma'ana a sanya liman a tsakiya, saboda fadin Annabi s.a.w. "Masu hankali daga cikinku, su bi bayana" kamar yadda Muslim ya rawaito a hadisi mai lamba ta : 116. sannan da fadin Anas RA lokacin da yake bada labarin ziyarar da Annabi s.a.w. ya kai gidansu : " Sai muka tsaya ni da marayan a bayansa" kamar yadda Bukhari ya rawaito a hadisi mai lamba ta :694, daga nan kuma sai a cigaba da cika shi ta bangaren dama.
Haka nan ake so sahu na biyu shi ma ya kasance, ya fara daga tsakiya ya tafi zuwa dama, saboda fadin Bara'u dan Azib RA "Mun kasance idan muka yi sahu a bayan Annabi s.a.w. mu kan so mu kasance a damansa, ya fuskanto mu da fuskarsa " Muslim a hadisi mai lamba ta : 709.
Allah ne mafi sani
Jamilu Zarewa
21\2\2015
TA YI ALWALA DA RUWAN FITSARI, HAR TA YI SALLAH BA TA SANI BA
TAMBAYA:
Nakasan ce lokacin da Ina bording school idan senior na ya aikeni debo ruwa kafin na kawo masa ruwan sai nayi fitsari acikin rowan, kuma ban san adadin mutanen dana yiwa hakan ba, saboda ganin yadda senior yin mu suke gallaza mana da sunan seniority ga shi yanzu ban san inda zan gansu ba ballantana na nemi afuwar su, me ya kamata na yi kenan a yanzun? nagode, Allah ya kara maka imani da ilmi mai amfani
Amsa :
To 'yar'uwa ina rokon Allah ya kare mu daga irin wannan danyan aikin, Allah ya sa su kuma shawagabannin makarantu su kula da irin wannan cin zalin, ina baki shawara ki yawaita istigfari, mutukar lokacin da kika yi hakan kin balaga, su kam sallarsu da wankansu sun inganta, saboda a zance mafi inganci na malamai duk wanda ya yi alwala da ruwa mai najasa, bai kuma gano hakan ba, sai bayan lokacin sallar ya fita, to ba zai sake sallar ba, haka ma wanda ya yi wankan janaba, saboda addinin musulunci addini ne mai sauki.
Allah ne mafi sani
.
Duba Al'ausad na Ibnul- munzir shafi na 18 .
Jamilu zarewa
14\2\2015
ZAMAN GULMAR SHUWAGABANNI DA 'YAN SIYASA
Tambaya :
Assalãmu Alaykum, Yaa Shaykh, menene hukuncin magana akan shugabanni da 'yan siyasa? Shi ma gulma ne ko akwai banbanci idan mutumin yana da nauyin yiwa al'umma shugabanci da hidima? Jazakumullahu Khayran
Amsa :
To dan'uwa Allah da manzonsa sun haramta cin naman mutane, sannan malamai suna cewa : gulmar shuwagabanni da malamai ta fi tsananin haramci , saboda cin naman shuwagabanni zai jawo ayi musu tarzoma, kamar yadda cin naman malami zai jawo a raina ilimi, saidai akwai wuraren da ya halatta a ci naman mutane saboda maslaha, kamar idan aka zalunci mutum to ya halatta idan zai kai kara ya bayyana zaluncin da aka yi masa, haka nan idan ya ga wani sharri yana so a taimaka masa wajan gusar da shi to ya halatta ya fadi sunan mai laifin, kamar yadda kuma ya hallata ayi gulmar mutumin da ya shahara da aikata sabo da fasikanci, don a guji sharrinsa. Duba Azkar : 489 da kuma Majmu'ul fataawa 28\221 .
A bisa abin da ya gabata za mu fahimci cewa : duk kasar da ake kafa shugaba ta hanyar zabe, to ya hallata mutane su tattauna matsalolin shugaban da yake kai, domin tunanin kawo canji a zabe mai zuwa, musamman idan shugaban ya kasance azzalumi kuma fasiki mai yawan aikata sabo, saidai ya wajaba maganar ta su ta zama gwargwadon bukata.
Allah ne mafi sani.