تسجيل الدخول

مشاهدة النسخة كاملة : الدرس الأول: مقدمات في فقه الطهارة


عبد الله الداخل
_19 _April _2013هـ الموافق 19-04-2013م, 12:28 AM
بسم الله الرحمن الرحيم

زاد المتفقه

الدرس الأول: مقدمات في فقه الطهارة

إن الحمد لله نحمده ونستعينه ونستغفره ونعوذ بالله من شرور أنفسنا ومن سيئات أعمالنا ، من يهده الله فلا مضل له ومن يضلل فلا هادي له، وأشهد أن لا إله إلا الله وحده لا شريك له وأشهد أن محمداً عبده ورسوله صلى الله عليه وعلى آله وصحبه ومن تبعهم بإحسان إلى يوم الدين وسلَّم تسليماً كثيراً.
أما بعد:
فإن الفقه في الدين فضيلة عظيمة، ومنقبة كريمة، من تحلى بها كان ممن أراد الله بهم خيراً ؛ كما صحَّ عن النبي صلى الله عليه وسلم أنه قال: (( من يرد الله به خيراً يفقِّهْهُ في الدين )) متفق عليه من حديث معاوية بن أبي سفيان رضي الله عنه.
وكان فقهه في الدين من أسباب خيريته ورفعته، كما في الصحيحين من حديث أبي هريرة رضي الله عنه أن النبي صلى الله عليه وسلم قال: ((خياركم في الجاهلية خياركم في الإسلام إذا فَقُهوا )).
وقال: ((خياركم إسلاماً أحاسنكم أخلاقاً إذا فَقُهوا )) رواه الإمام أحمد والبخاري في الأدب المفرد من حديث أبي هريرة رضي الله عنه، وصححه الألباني.
وقال النبي صلى الله عليه وسلم: (( خصلتان لا تجتمعان في منافق: حسن سمت وفقه في الدين)). رواه الترمذي من حديث أبي هريرة رضي الله عنه.
والفقه في الدين يشتمل علىفقه كتاب الله تعالى وما جاء به النبي صلى الله عليه وسلم من أمور الاعتقاد والعبادات والمعاملات والآداب وغيرها من أمور الدين.
ومنه ما هو فرض عين: وهو ما يصح به إسلام العبد وما يتوقف عليه أداء العبادات الواجبة واجتناب ما حرم الله.
ومنه ما هو فرض كفاية على الأمة: إذا قام به من يكفي سقط الإثم عن الباقين لقوله تعالى: {وما كان المؤمنون لينفروا كافة فلولا نفر من كل فرقة منهم طائفة ليتفقهوا في الدين ولينذروا قومهم إذا رجعوا إليهم لعلهم يحذرون}
وقد دلت هذه الآية على أن العلم الشرعي سبب للنجاة من سخط الله وعقابه؛ وأن من العلم ما يجب على العبد تعلمه ليحذر من عقاب الله وينجو منه، وأن من لم يكن من الفقهاء فإنه يجب عليه أن يسأل أهل الفقه عما يشكل عليه من أمر دينه، ويجب عليه أن يستجيب لما يُنذر به، ويحذَر مما يُحذَّر منه.
ولأهمية مسائل الاعتقاد أفردها الأئمة في مصنفات قيّمة جامعة، وأفردوا مسائل فقه الأحكام الشرعية في مصنفات أخرى تيسيراً على طلبة العلم.
وينبغي لطالب العلم أن يأخذ بحظ وافر من التفقه في الدين عقيدة وشريعة وأن يعتني بحفظ أدلة المسائل من الكتاب والسنة ويتفقه في معانيها وأحكامها ، وأن يسيرَ في ذلك على طريقة أهل العلم والإيمان، وأن يتبع سبيلهم، ولا يبتدعَ طريقة تخالف طريقتهم، ولا يسلك منهجاً غير منهجهم؛ فما أجمعوا عليه فهو حجة قاطعة لقول الله تعالى: {ومن يتبع غير سبيل المؤمنين نولّه ما تولّى ونصله جهنم وساءت مصيراً}.
وما اختلفوا فيه فمردّه إلى الكتاب والسنة ، كما قال الله تعالى: {وما اختلفتم فيه من شيء فحكمه إلى الله} وقال: {ولو ردوه إلى الرسول وإلى أولي الأمر منهم لعلمه الذين يستنبطونه منهم}
وهذا وعد من الله تعالى أنه يوفق بعض عباده لمعرفة الحق في ذلك.

ومن طلب الهدى من الله صادقاً هداه الله، ومن توكل على الله كفاه، ومن أوى إليه آواه، {ومن يعتصم بالله فقد هدي إلى صراط مستقيم}، ومن علامة الاعتصام بالله اتباع سنة النبي صلى الله عليه وسلم وأصحابه.

وقد جرت عادة أهل العلم على ترتيب مسائل فقه العبادات على ترتيب أركان الإسلام وقدموا كتاب الطهارة على كتاب الصلاة لأن الطهارة شرط من شروط الصلاة ، وألحقوا بكتاب الطهارة ما يتصل بها من مسائل تيسيراً على المتعلمين.

كتاب الطهارة

الطهارة على قسمين: طهارة معنوية وطهارة حسية
فأما الطهارة المعنوية: فهي تزكية النفس من الكفر والفسوق والعصيان؛ قال الله تعالى: {إنما يريد الله ليذهب عنكم الرجس أهل البيت ويطهركم تطهيراً}
وقال تعالى: {خذ من أموالهم صدقة تطهرهم وتزكيهم بها}
وقال تعالى: {وإذا سألتموهن متاعاً فسألوهن من وراء حجاب ذلكم أطهر لقلوبكم وقلوبهن}
فالطهارة في هذه الآيات هي الطهارة المعنوية من رجس الذنوب وأوضار المعاصي ورين الغفلة.
وأعظم ذلك الطهارة من الشرك والبدعة، ولذلك شرع للمتوضئ أن يدعو بما ورد؛ ففي صحيح مسلم من حديث عمر بن الخطاب رضي الله عنه عن النبي صلى الله عليه وسلم أنه قال: (( ما منكم من أحدٍ يتوضأ فيبلغ الوضوء أو فيسبغ الوضوء ثم يقول أشهد أن لا إله إلا الله وحده لا شريك له وأشهد أن محمداً عبده ورسوله إلا فتحت له أبواب الجنة الثمانية يدخل من أيها شاء)).
فشهادة أن لا إله إلا الله طهارة من الشرك، وشهادة أن محمداً رسول الله صلى الله عليه وسلم طهارة من البدعة، ومن جمع بين التوحيد واتباع السنة كان من أهل الجنة.

وأما الطهارة الحسية فهي النقاء من النجاسات؛ فكل ثوب وبقعة نقية من النجاسات فهي طاهرة؛ هذا من حيث المعنى اللغوي.
وأما المعنى الشرعي للطهارة فهو: ارتفاع الحدث وزوال الخبث حقيقة أو حكماً.
والحدَث: هو معنى يحدث بالبدن تنتقض به الطهارة.
والحدَث على نوعين:
النوع الأول: الحدث الأكبر، وهو الذي يكون بسبب الجنابة والحيض والنفاس، والتطهر منه يكون بالاغتسال بعد زوال المانع؛ فإذا طهرت الحائض والنفساء وجب عليها الاغتسال للصلاة، وكذلك الجنب بسبب جماع أو إنزال الماء باحتلام أو غيره يجب عليه الاغتسال للصلاة؛ لأن الصلاة لا تصحّ بغير طهارة، ولا يجوز تأخير الصلاة عن وقتها.
والمحدِث حدثاً أكبر لا يحلّ له أن يصلي ولا أن يمسّ المصحف ولا أن يمكث في المسجد إلا عابر سبيل حتى يغتسل.

والنوع الآخر: الحدث الأصغر كالخارج من السبيلين والنوم، ويرتفع هذا الحدث بالوضوء.
وارتفاع الحَدَث شرط لصحة الصلاة، لقول النبي صلى الله عليه وسلم: (( لا يقبل الله صلاة أحدكم إذا أحدث حتى يتوضأ)). متفق عليه من حديث أبي هريرة رضي الله عنه.
وفي رواية في صحيح البخاري: قال رجل من حضرموت: وما الحدَثُ يا أبا هريرة؟
قال: (فُسَاء أو ضراط).
أَحْدَثَ أي: حصل منه الحدَث الذي ينتقض به الوضوء.
وتفسير أبي هريرة هو من باب التمثيل، والتنبيه بالأخف على الأغلظ.
والفُسَاء هو الريح التي تخرج بلا صوت يسمع.
والضُّراط ما كان مع صوت مسموع.
وفي صحيح مسلم من حديث ابن عمر رضي الله عنهما قال: سمعت رسول الله صلى الله عليه وسلم يقول: (( لا تُقبل صلاة بغير طُهور، ولا صدقة من غلول)).
الطُّهور بضمّ الطاء: التطهر من الحدث والخبث.
والطَّهور بفتح الطاء هو ما يُتَطهَّر به من الماء وغيره، قال الله تعالى: {وأنزلنا من السماء ماء طَهوراً}.

والخَبَثُ هو النجاسة، وزوالها عند القدرة على ذلك شرط لصحة الصلاة.
فالنجاسة إذا كانت على البدن أو الثياب أو البقعة التي يصلى عليها وجبت إزالتها على القادر على ذلك؛ فإن تعذَّرت إزالتها ولو بتأخير الصلاة إلى آخر وقتها جاز له أن يصلي على حاله؛ كالمريض والأسير المقيّد وغيرهما ممن لا يستطيع تطهير نفسه من النجاسة ؛ فإنهم يصلّون على حالهم.

والنجاسة على نوعين:
النوع الأوَّل: النجاسة المعنوية، وهي النجاسة التي وصفت بها الأعمالُ الخبيثة، وأسبابها، ومن يقوم بها، كما قال الله تعالى: {إنما المشركون نجس}، وقال في المنافقين: {فأعرض عنهم إنهم رجس} وقال في الزناة: {الخبيثات للخبيثين والخبيثون للخبيثات}
وقد عدَّ النبيُّ صلى الله عليه وسلم الزنا ومقدماته من القاذورات، فقال: ((اجتنبوا هذه القاذوراتِ التي نهى الله تعالى عنها؛ فمن ألمَّ بشيء منها؛ فليستترْ بستر الله، و ليتب إلى الله؛ فإنه مَن يُبْدِ لنا صفحتَه نُقِمْ عليه كتابَ الله)). رواه الحاكم والبيهقي من حديث ابن عمر، وقد حسَّنه العراقي، وصححه الألباني، وهو في الموطأ أيضاً من مرسل زيد بن أسلم.
فالشرك والنفاق والزنا والفجور من الأعمال الخبيثة ، وصاحبها خبيث بسبب ما ارتكبه من الأعمال الخبيثة، لكن نجاسته معنوية ليست بحسية، والتطهر من هذه النجاسات إنما يكون بالتوبة والإيمان؛ فإذا تاب وآمن فهو مؤمن طاهر من هذه الأعمال الخبيثة؛ كالثوب إذا غسل وطهر لم يعد للنجاسة فيه أثر.
والمعاصي كلها لها نصيب من وصف النجاسة ، وإن كانت النجاسات على درجات فليست نجاسة الشرك كنجاسة معاصي المسلمين، وليست نجاسة الكبائر كنجاسة الصغائر واللَّمَم.
بل إنَّ التطهُّرَ المعنويَّ يُشْرَعُ من رَيْنِ الغفلة وغَيْنِ القلبِ، ولذلك كان من دعاء النبي صلى الله عليه وسلم في استفتاح الصلاة: (( اللهم نقني من خطاياي كما يُنقَّى الثوب الأبيض من الدَّنَس، اللهم اغسلني من خطاياي بالثلج والماء البارد)). متفق عليه من حديث أبي هريرة رضي الله عنه.
ويسنُّ للمؤمن أن يدعو بهذا الدعاء ليجمع بين طهارة الروح والبدن.

النوع الثاني: النجاسة الحسّية، وهي كل مادّة محسوسة حَكَم الشرع بنجاستها لذاتها لا لوصفها المعنوي؛ كالبول، والحيض، والكلب، والخنزير، والميتة.
والنجاسة الحسية على قسمين:
القسم الأول: النجاسة العينية، والمراد بها الأعيان النجسة كالتي سبق التمثيل بها.
والقسم الثاني: النجاسة الحُكْمية، وهي الأعيان الطاهرة التي نجَّسَتها الأعيان النجسة.
مثال ذلك: الثوب المنسوج من خيوط طاهرة؛ إذا وقعت عليه نجاسة فحكمه أنه نجس؛ فإذا أزيلت النجاسة حُكِم بأنه طاهر.
والفرق بين النجاسة العينية والنجاسة الحكمية: أن النجاسة العينية لا يمكن تطهيرها؛ فالكلب لو غسل مائة مرة فهو نجس عين لا يطهر أبداً.
وأما الإناء الذي ولغ فيه الكلب فهو إناء نجس حُكماً لا عيْناً؛ فإذا غُسِلَ سبع غسلات إحداها بالتراب حكم بطهارته.

الفرق بين الوسخ والنجاسة:
ومما ينبغي أن يُعلم أنه ليس كلّ وَسَخ نجاسة؛ فما يكون على الثوب من أثر الغبار والعرق وتغير لونه بذلك أو ببعض الأصباغ الطاهرة لا يجعله ثوباً نجساً؛ بل هو طاهرٌ وإن لم يكن نظيفاً.

وبارتفاع الحدَث وزوال الخبَث تتحقق الطهارة .

حكم الطهارة:
والطهارة واجبة إذا حضر ما تجب له الطهارة؛ وأعظم ذلك الصلاة؛ قال النووي: (أجمعت الأمّة على أن الطهارة شرط في صحة الصلاة).
فإذا حضرت الصلاة وجب على المحدث أن يتطهّر ، ولا يجوز له أن يؤخّر الصلاة عن وقتها، وكذلك إذا أراد الجنب أن يمكث في المسجد وجب عليه أن يغتسل، ولا يحلّ له أن يمكث في المسجد وهو جنب إلا عابر سبيل ؛ كأنْ يدخل من باب ويخرج من باب لحاجته إلى ذلك.
ومن كان في وقته فسحة فله أن يؤخّر التطهر من الحدث إلى حين الوقت الذي يجب فيه التطهر؛ كالذي يحتلم في أوّل النهار فله أن يؤخّر التطهر – إن شاء- إلى حين وجوب صلاة الظهر.

شروط وجوب الطهارة:
والطهارة من الحدث واجبة على كل محدِثٍ، بالغ، عاقل، قادر على التطهّر، عالمٍ بوجوب الطهارة وكيفية التطهر.
فأمّا غير المحدث فلا يجب عليه أن يعيد التطهّر إذا حضرت الصلاة وهو على وضوء سابق لم ينتقض.
وأمّا غير البالغ؛ فلا يجب عليه التطهّر من الحدث لعدم تكليفه بالأحكام الشريعة؛ فإن كان مميّزاً صحّ منه التطهّر وأثيب عليه إن فعله؛ ويستحبّ لوليّه أن يعوّده على الصلاة والتطهّر لها.
وأمّا غير العاقل وهو المجنون ومن ذهب عقله لعلّة فإنه لا يجب عليه التطهّر حتى يرجع إليه عقله؛ لأن حضور العقل شرط في التكليف بأحكام الشرع.
وأمّا غير القادر على التطهّر لمرضٍ أو عجزٍ ونحوهما فإنّه يخفف عنه فإن كان قادراً على التيمم تيمّم وإن لم يقدر عليه صلّى على حاله، ويعتبر طاهراً حكماً.
وأمّا الجاهل الذي لا يعلم بوجوب الطهارة كمن نشأ في مكان فيه جهل عظيم بأحكام الدين أو أسلم حديثاً ولم يعلم بما يوجب الحدث وما يرفعه ؛ فإنّه يُعذر بجهله؛ لأن الله تعالى لا يعّذب أحداً لم تقم عليه الحجة الرّسالية كما قال تعالى: {وما كنّا معذبين حتى نبعث رسولاً}
ويجب عليه أن يتفقّه في الدين ما استطاع ، ويجب على من يعلم بحاله من المسلمين أن يعلّمه ويرشده.
وكذلك يقال في الذي يعلم بوجوب التطهّر لكنه لا يدري كيف يتوضّأ، ولا كيف يغتسل الاغتسال الصحيح.
وهذا قد يقع لبعض الناس إذا قلّ العلم وانتشر الجهل، وعلى الفقيه أن يكون عالماً بأحكام هؤلاء عند الحاجة إليه في الفتوى والتعليم.

شروط صحّة الطهارة:
وأمّا شروط صحّة الطهارة فهي: الإسلام، والعقل، والتمييز، والنيّة، وزوال ما يمنع الطهارة مع القدرة، والإتيان بالقدر المجزئ من التطهّر، ودخول الوقت لمن كان حدثه دائماً.
فأما اشتراط الإسلام فذلك لأن الطهارة عبادة والعبادة لا تصحّ من الكافر حتّى يسلم.
وأما العقل فلأن من لا عقل له لا نيّة له.
وأمّا التمييز فلأن الصغير غير المميّز لا تصح منه النية.
وأمّا النية فلأن الوضوء عمَل ولا يصحّ العمل إلا بنيّة، لقول النبي صلى الله عليه وسلم: ((إنما الأعمال بالنيات)). فهي شرط في الوضوء والاغتسال والتيمم؛ وأمّا إزالة النجاسة فلا يشترط لها النيّة لأنها من باب التروك؛ أي ما يُطلب تركه والتخلّص منه.
والنيّة محلها القلب، والتلفّظ بها بدعة.
وأمّا زوال ما يمنع التطهّر فله أمثلة: منها الحيض والنفاس ؛ فلا يصحّ تطهّر المرأة حتى تطهر من حيضها ونفاسها، ومن توضّأت وهي حائض لم يصحّ منها.
ويستثنى من ذلك الجنب إذا أراد النوم فإنّه يسنّ له أن يتوضأ للحديث الصحيح في ذلك، لكنّه لا يصلّي بهذا الوضوء حتى يغتسل.
وكذلك من وضع شيئاً يمنع وصول الماء إلى البشرة في مواضع الوضوء فإنه يجب عليه إزالته إلا ما وردت الرخصة فيه كالخفّين والجبيرة واللصوق التي توضع على الجروح ونحوها.
وأمّا الإتيان بالقدر المجزئ من التطهّر فيأتي بيانه في الدروس القادمة إن شاء الله تعالى.
وأما دخول الوقت فهو شرط صحّة لمن كان حَدَثُه دائماً كالمستحاضة ومن به سلَس بول ونحوهما فهؤلاء يتوضؤون لكل صلاة ثم يصلون ولو استمرّ الحدث معهم ولم ينقطع بعد الوضوء كما سيأتي بيانه في الدروس القادمة إن شاء الله تعالى.

ما تحصل به الطهارة:
يتلخّص مما سبق بيانه أن الطهارة من الخبث تكون بإزالته عند القدرة على ذلك، وأن الطهارة من الحدث الأكبر تكون بالاغتسال، وأن الطهارة من الحدث الأصغر تكون بالوضوء، فمن لم يجد الماء أو عجز عن استعماله فليتيمم؛ فإن عجز عنهما صلّى حاله ويكون طاهراً حُكْماً.

ما تشترط له الطهارة:
أجمع أهل العلم على أن الطهارة من الحدثين شرط لصحّة الصلاة، واختلفوا في مسّ المصحف والطواف بالبيت للمحدث حدثاً أصغر.
وسيأتي بيان هذه المسائل في مواضعها إن شاء الله تعالى، وإنما المقصود في هذا الدرس الإلمام بالأحكام العامة للطهارة، والله الموفّق والهادي إلى سواء السبيل.

طاهر جبريل دكو
_3 _May _2013هـ الموافق 3-05-2013م, 05:52 PM
Darasina daya shimfida gameda fahimtar dahara
Da sunan Allah mai rahama mai jinkai.
Guzurin mai neman (neman ilimin) fiqihu
Darasi na daya: Gabatarwa cikin fikihun tsarki
Lallai dukkanin godiya sun tabbata ga Allah, muna gode maSa, muna neman taimakonSa, muna neman gafararSa, kuma muna neman tsarin Allah daga sharrurrukan kawukanmu da munanan ayyukanmu. Duk wanda Allah Ya shiryar dashi babu mai batardashi, kuma duk wanda Ya batar, babu mai shiryardashi, kuma ina shaidawa babu abin bawtawa da gaskiya sai Allah, Shi kadai Yake baShida abokin tarayya, kuma ina shaidawa lallai Muhammadu bawanSa ne kuma ManzonSa, tsira da amincin Allah su tabbata agareshi da alayensa da sahabbansa da wadanda suka biyo bayansu da kyawtatwa har zuwa ranar sakamako da aminci aminci mai yawa.
Bayan haka:
Lallai fahimtar addini falalace mai girma, kuma matsayine madawkaki, duk wanda yayi ado dashi, ya kasance cikin wadanda Allah Yake nufinsu da alheri, kamar yadda ya inganta daga Annabi (tsira da amincin Allah su tabbata agareshi) yace:
(( من يرد الله به خيراً يفقِّهْهُ في الدين )) متفق عليه من حديث معاوية بن أبي سفيان رضي الله عنه.
Ma’ana:”Wanda Allah ke nufinsa da alheri, yana fahimtaddashi addini” Bukhari da Muslim ne suka ruwaitoshi daga hadisin Mu’awiya Dan Abu Sufiyan (Allah Ya kara musu yarda)
Kuma fahimtansa (wato bawa) ga addini yana daga cikin sabubban alherinsa da dawkakarsa, kamar yadda yazo acikin sahihul Bukhari da Muslim daga hadisin Abu Huraira (Allah Ya kara masa yarda) lallai Annabi ((tsira da amincin Allah su tabbata agareshi) yace:
((خياركم في الجاهلية خياركم في الإسلام إذا فَقُهوا )).
Ma’ana:”Zababbun cikinku a (zamanin) jahiliyya, sune Zababbun cikinku a musulunci idan suka fahimci (addini). Kuma yace:
((خياركم إسلاماً أحاسنكم أخلاقاً إذا فَقُهوا )) رواه الإمام أحمد والبخاري في الأدب المفرد من حديث أبي هريرة رضي الله عنه، وصححه الألباني.
Ma’ana:”Mafi alherin cikinku amusulunci, sune wadanda suka fi kyawawan hali acikinku idan suka fahimci (addini). Imamu Ahmad da Imamul Bukhari (acikin adabul mufrad) ne suka ruwaitoshi daga hadisin Abu Huraira (Allah Ya kara masa yarda) kuma Albani ya ingantashi.
Kuma Annabi (tsira da amincin Allah su tabbata agareshi) yace:
(( خصلتان لا تجتمعان في منافق: حسن سمت وفقه في الدين)). رواه الترمذي من حديث أبي هريرة رضي الله عنه.
Ma’ana:”Dabi’u guda biyu basu haduwa ga munafiki, kyawun dabi’a da fahimtan addini” Imamu-Ttirmizi ne ya ruwaitoshi daga hadisin Abu Huraira (Allah Ya kara masa yarda).
Kuma fahimtar addini ya hadada fahimtar littafin Allah (Madawkakin Sarki) da abubuwanda Annabi (tsira da amincin Allah su tabbata agareshi) yazo dasu daga al’amuran akida da ibada da mu’amala da ladubba da sawransu daga al’amuran addini.
Kuma daga cikinsu (wato ilimin addini) akwai wanda yake matsayin farilla akan kowa (wato wacce kowa shi yakeyiwa kansa wani baya dawkewa wani) shine: wanda musuluncin bawa ke inganta dashi da kuma abinda aiwatar da wajibi da nisantan abinda Allah Ya haramta baya yuwuwa sai da shi.
Daga cikinsu akwai farlu kifaya akan al’umma-ma’ana- idan wasu suka aikatashi bisa wadatarwa, zunubi ya sawka daga sawran jama’a, saboda fadin Allah (Madawkakin Sarki):
{وما كان المؤمنون لينفروا كافة فلولا نفر من كل فرقة منهم طائفة ليتفقهوا في الدين ولينذروا قومهم إذا رجعوا إليهم لعلهم يحذرون}
Ma’ana:”kuma baya kasancewa ga muminai su fita zuwa yaki gaba daya. Saboda haka, don menene wata jama’a daga garesu bata fita (zuwa neman ilimi ba) domin su nemi ilimin fahimtar addini kuma domin suyi gargadi ga mutanensu idan sun komo zuwa garesu tsammaninsu su daw izna”.
Hakika wannan ayar tayi nuni zuwaga cewa lallai ilimin shari’a sababine na tsira daga fushin Allah da ukubasSa, kuma cewa lallai daga cikin ilimi akwai wanda saninsa ke wajaba akan bawa saboda ya kiyaye (kansa) daga ukubar Allah kuma ya tsira daga gareshi (wato ukubar), kuma cewa duk wanda bai kasance daga cikin masu fahimtar addiniba, to ya wajaba agareshi ya tambayi malaman fikihu gameda abinda ya shiga masa duhu cikin al’amuran addini, kuma ya wajaba agareshi ya karbi gargadinda ake yi masa kuma ya kiyaye daga abinda ake tsawratardashi daga gareshi.
Saboda muhimmancin mas’alolin akida, sai malamai suka kebancesu cikin rubuce rubuce masu kima (kuma) wadanda suka game, kuma sun kebance mas’aloli na fikihun hukunce hukuncen shari’a acikin wasu rubuce rubucen domin sawwakewa daliban ilimi.
Kuma ya kamata dalibin ilimi ya riki wani kaso mai girma daga ilimin addini (abinda ya shafi) akida da (hukunce hukuncen) shari’a, kuma ya kula da haddan dalilai gameda mas’aloli daga Alqur’ani da Sunna kuma ya yi kokari wurin fahimtar ma’anoninsu da hukunce hukuncensu, kuma ya bi tafarkin ma’abuta ilimi da imani acikin hakan, kada ya kirkiri wata hanya da ta sabawa tasu, kuma kada ya dawki wani tsari sabanin tsarinsu, duk abinda suka yi ijima’i akai, to hujjane yankakke saboda fadin Allah (Madawkakin Sarki):
{وَيَتَّبِعْ غَيْرَ سَبِيلِ الْمُؤْمِنِينَ نُوَلِّهِ مَا تَوَلَّى وَنُصْلِهِ جَهَنَّمَ وَسَاءَتْ مَصِيرًا}.
Ma’ana:”… kuma yabi sabanin tafarkin muminai, zaMu jibinta masa abinda ya jibinta kuma Mu shigar dashi Jahannama, kuma ta munana (ga zama) makoma”.
Abinda sukayi sabani acikinsa kuma, to makomarsa (don tantancewa) shine Alqur’ani da Hadisi kamar yadda Allah Yace:
{ وَمَا اخْتَلَفْتُمْ فِيهِ مِنْ شَيْءٍ فَحُكْمُهُ إِلَى اللَّهِ }
Ma’ana:”Duk abinda kukayi sabani acikinsa, to hukuncinsa naga Allah”
Kuma Yace:
{ وَلَوْ رَدُّوهُ إِلَى الرَّسُولِ وَإِلَى أُولِي الْأَمْرِ مِنْهُمْ لَعَلِمَهُ الَّذِينَ يَسْتَنْبِطُونَهُ مِنْهُمْ }
Ma’ana:”…Kuma da sun mayar dashi zuwaga Manzon (Allah) kuma zuwaga ma’abuta al’amari daga cikinsu, da wadanda suke bincikensa daga cikinsu (wato malamai) zasu sanshi”
Wannan alkawarine daga Allah (Madawkakin Sarki) cewa lallai Yana datarda wasu daga cikin bayinSa zuwaga fahimtar gaskiya.
Kuma wanda ya nemi shiriya daga Allah bisa gaskiya, Allah zai shiryar dashi. kuma wanda ya dogara ga Allah, Allah ya isar masa, wanda ya nemi mafaka awurin Allah, Allah zai bashi, “kuma duk wanda yayi riko ga Allah, hakika an shiryar dashi zuwa tafarki madaidaici” kuma yana daga cikin alamomin riko ga Allah, bin sunnar Annabi (tsira da amincin Allah su tabbata gareshi) da sahabbansa.
Hakika al’adar ma’abuta ilimi ta gudana akan rattaba mas’alolin fikihu bisa tartibin rukunnan musulunci, kuma sun gabatarda littafin tsarki akan littafin salla saboda tsarki yana daga cikin sharuddan salla, kuma duk abubuwanda keda alaka da tsarki suka riskardashi ga littafin tsarki saboda sawwakewa ga masu neman ilimi.
Littafin dahara:
Dahara (wato tsarki) iri biyune: tsarki na ma’ana (wanda yake da alaka da sifa kamar tsarkaka daga miyagun ayyuka) da dahara ta hissi (wato wacce ake iya shaida samuwarta a zahiri).
Dahara ta ma’ana itace: tsarkake rai daga kafirci da fasikanci da sabon (Allah). Allah (Madawkakin Sarki) Yace:
{إِنَّمَا يُرِيدُ اللَّهُ لِيُذْهِبَ عَنْكُمُ الرِّجْسَ أَهْلَ الْبَيْتِ وَيُطَهِّرَكُمْ تَطْهِيرًا}
Ma’ana:”Allah na nufin Ya tafiyar da kazantace kawai daga gareku yaku mutanen babban gida! Kuma Ya tsarkakeku tsarkakewa”. Kuma (Madawkakin Sarki) Yace:
: { خُذْ مِنْ أَمْوَالِهِمْ صَدَقَةً تُطَهِّرُهُمْ وَتُزَكِّيهِمْ بِهَا }
Ma’ana:”Ka karbi sadaka daga dukiyoyinsu ka tsarkakesu (daga zunubi) kuma ka tabbatar da kirkinsu da ita…” Kuma (Madawkakin Sarki) Yace:

{وَإِذَا سَأَلْتُمُوهُنَّ مَتَاعًا فَاسْأَلُوهُنَّ مِنْ وَرَاءِ حِجَابٍ ذَلِكُمْ أَطْهَرُ لِقُلُوبِكُمْ وَقُلُوبِهِنَّ}
Ma’ana:”Kuma idan zaku tambayesu wadansu kaya, to ku tambayesu daga bayan shamaki. Wannan shi yafi tsarki ga zukatanku da zukatansu…”
Don haka dahara acikin wadannan ayoyin itace dahara ta ma’ana, (wato tsarkaka) daga dawdar zunubbai da kazanta ta sabon (Allah) da tsatsar gafala.
Mafi girma daga haka (wato tsarki na ma’ana) shine tsarkaka daga shirka da bidi’a, wannan shi yasa aka shar’antawa mai alwala yin addu’a da addu’ar da tazo acikin sahihu Muslim daga hadisin Umar Dan Khaddabi (Allah Ya kara masa yarda) daga Annabi (tsira da amincin Allah su tabbata gareshi) yace:
(( ما منكم من أحدٍ يتوضأ فيبلغ الوضوء أو فيسبغ الوضوء ثم يقول أشهد أن لا إله إلا الله وحده لا شريك له وأشهد أن محمداً عبده ورسوله إلا فتحت له أبواب الجنة الثمانية يدخل من أيها شاء)).
Ma’ana:”Babu daya daga cikinku wanda zaiyi alwala saiya kyawtata alwalar, sannan yace; na shaida babu abin bawtawa da gaskiya sai Allah Shi kadai Yake baShida abokin tarayya, kuma na shaida cewa lallai Muhammadu bawanSane kuma ManzonSane, face an bude masa kofofin aljanna guda takwas ya shiga duk ta inda yaso”.
Saboda haka shaidawa babu abin bawtawa da gaskiya sai Allah, tsarkakane daga shirka, shaidawa lallai Muhammadu Manzon Allahne kuma tsarkakane daga bidi’a, wanda ya hada tsakanin kadaita Allah da bin sunnar Annabi (tsira da amincin Allah su tabbata agareshi) zai kasance daga cikin yan aljanna.
Amma ita dahara ta hissi (wato ta zahiri) itace tsabtatuwa daga najasoshi, saboda haka dukkanin tufafi ko wurin daya tsarkaka daga abubuwan najasa, to yakasance mai tsarki kenan, wannan ta bangaren ma’ana kenan a harshen larabci.
Amma ma’anar dahara a shari’ance itace: dawkewar hadasi da gushewar khabasi bisa hakika ko hukunci.
Hadasi, wani abu ne na (ma’ana) dake faruwa ga jiki wanda alwala ke warwarewa sakamakon faruwarsa.
Kuma hadasi naw’i biyune:
Naw’i na farko: babban hadasi, shine wanda ke kasancewa sakamakon janaba ko haila ko biki. Tasrkaka daga gareshi yana kasancewane ta hanyar yin wanka bayan gushewar abinda ke hanawa. Saboda haka idan mai haila ta tsarkaka ko mai biki, to ya wajaba akanta tayi wanka don salla, hakama mai janaba sakamakon jima’i ko fitan maniyyi a mafarki ko waninsa, shima ya wajaba yayi wanka kafin yayi salla, saboda salla bata inganta batareda alwalaba kuma baya halatta a jinkirta salla daga barin lokacinta.
Wanda yayi babban hadasi, baya halatta gareshi yayi salla ko shafan Alkur’ani ko zama a masallaci face mai ketare hanya har sai yayi wanka.
Naw’i na biyun kuma shine: karamin hadasi, misali abinda ke fita daga mafita biyu (wato mafitsara da dubura), da bacci, to irin wannan hadasin yana gushewane idan akayi alwala.
Kuma gushewar hadasi sharadine gameda ingancin salla, saboda fadin Annabi (tsira da amincin Allah su tabbata agareshi):
(( لا يقبل الله صلاة أحدكم إذا أحدث حتى يتوضأ)). متفق عليه من حديث أبي هريرة رضي الله عنه.
Ma’ana:”Allah baYa karban sallar dayanku idan yayi hadasi har sai yayi alwala” Bukhari da Muslimne suka ruwaitoshi daga hadisin Abu Huraira (Allah Ya kara masa yarda). A wata riwayar da tazo cikin sahihul bukhari, wani mutum daga Hadara mawt yace: ya kai Abu Huraira menene hadasi? (sai) yace: tusa mara kara da mai kara.
Lafazin [Ahdatha] yana nufi; faruwar hadasi - wanda shike warware alwala.
Amma fassarar Abu Huraira kawai yayi tane a babin misali da fadakarwa dangane da (hadasi) maafi sawki (wato tusa) saboda a fahimci shigan mafi tsananin (kamar bayan gari da bawali)
[Alfusa’u] (a harshen larabci) yana nufin tusar da take fita ba tareda anji karar fitantaba.
Shi kuma [Adduradu] shine mai kara.
Yazo acikin sahihu Muslim daga hadisin dan Umar (Allah Ya kara musu yarda) yace; naji Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata agareshi) yana cewa:
(( لا تُقبل صلاة بغير طُهور، ولا صدقة من غلول)).
Ma’ana:”Ba’a karban sallar da akayita batareda alwalaba, hakananma sadaka daga barawo”
Lafazin ((Adduhuru)) (da rufu’a) yana nufin tsarkaka daga hadasi ko khabasi.
Shi kuma ((Addahuru)) (da fataha) yana nufin abinda ake tsarkin dashi kamar ruwa da waninsa. Allah (Madawkakin Saarki) yace:
{وأنزلنا من السماء ماء طَهوراً}.
Ma’ana:”Kuma mun sawkar da ruwa mai tsakakewa daga sama”
Kuma (lafazin) ((Alkhabasu)) yana nufin najasa, kuma gusar dashi ahalin samun iko sharadine na ingancin salla.
Saboda haka najasa idan ta kasance ajiki ko atufafi ko awurin salla, to ya wajaba a gusar da ita, ga wanda keda iko akan hakan. Idan gusar da ita ya ta’azzara ( koda da jinkirta salla zuwa karshen lokacin tane), to ya halatta yayi salla akan yanayin dayake (na rashin tsarki) kamar mara lafiya, da wanda yake tsare (a kurkuku) kuma adware, da waninsu cikin wadanda bazasu iya tsarkake kansuba daga najasa, to sukam sai suyi salla a halinda (suka samu kawukansu)
Kuma najasa naw’i biyune:
Naw’i na daya: najasa ta ma’ana, itace wacce ake sifanta munanan ayyuka da sabubbansu da mai aikatasu da ita. Kamar yadda Allah (Madawkakin Sarki) Yace:
{إنما المشركون نجس}،
Ma’ana:”Kawai (abin sani) mushirikai najasace…” Kuma Yace gameda munafukai:
{فأعرض عنهم إنهم رجس}
Ma’ana:”Saboda haka ka kawar da kai daga barinsu, lallai su kazantace…” Kuma yace gameda mazinata:
{الخبيثات للخبيثين والخبيثون للخبيثات}
Ma’ana:”Miyagun mata na miyagun mazane kuma miyagun maza na miyagun matane…”
Hakika Annnabi (tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi) ya kirga zina da abubuwanda ke kaiwa zuwa gareta daga cikin ayyukan kazanta, sai yace:
((اجتنبوا هذه القاذوراتِ التي نهى الله تعالى عنها؛ فمن ألمَّ بشيء منها؛ فليستترْ بستر الله، و ليتب إلى الله؛ فإنه مَن يُبْدِ لنا صفحتَه نُقِمْ عليه كتابَ الله)).
Ma’ana:”Ku nisanci wadannan ayyukan kazantar wadanda Allah Yayi hani gamedasu, duk wanda ya cudanya da wanin abu daga cikinsu, to ya suturtu da suturar Allah, kuma ya tuba zuwaga Allah, domin duk wanda ya bayyana mana sirrinsa, zamu tsayar masa da hukunci akan littafin Allah”.
Imam Al-Hakim da Imam Al-Bayhaki ne suka ruwaitoshi daga hadisin (Abdullahi) dan Umar kuma Iraki yace hadisine mai kyaw Albani kuma ya ingantashi, kuma yazo acikin muwadda daga Zaidu dan Aslam a matsayin mursal (wato tabi’i ya jingina shi ga Annabi ba tareda ambaton sahabi ba).
Saboda haka shirka da munafurci da zina da fajirci (duk) suna daga cikin miyagun ayyuka, kuma mai aikatasu shima mummunane (ga dabi’u) sakamakon abinda yake aikatawa na miyagun ayyuka, saidai najasarsa ta ma’anace ba wacce ake iya gani bace, kuma tsarkaka daga irin wannan najasar yana kasancewane kawai ta hanyar tuba da kuma imani. Idan ya tuba kuma yayi imani, to shi tsarkakakkene daga wadannan miyagun ayyukan, tamkar tufa idan aka wanketa aka tsarkaketa, zata dawo babu sawran tasirin najasar ajikinta.
Kuma dukkanin ayyukan sabo suna da wani kaso na sifan najasa, duk da cewa najasa tanada matakai (mabamabanta) saboda haka najasar shirka ba daidai takeba da najasar aikin da musulmi zaiyi na sabon (Allah) haka nanma najasar kaba’ira (manyan zunubbai) ba daidai take ba da najasar saga’ira (wato kananan zunubbai)
Bama haka kawaiba, lallai tsarkakuwa irinta ma’ana an shar’antata gameda tsatsar gafala da toshiyar zuciya, wannan shi yasa daga cikin addu’oin Annabi (tsira da amincin Allah su tabbata agareshi) a yayin fara salla:
(( اللهم نقني من خطاياي كما يُنقَّى الثوب الأبيض من الدَّنَس، اللهم اغسلني من خطاياي بالثلج والماء البارد)). متفق عليه من حديث أبي هريرة رضي الله عنه.
Ma’ana:”Ya Ubangijina, Ka tsarkakeni daga kurakuraina kamar yadda ake tsaftace farin tufafi daga dawda. Ya Ubangijina, Ka wankeni daga kurakuraina da kankara da ruwan sanyi” Bukhari da Muslimne suka ruwaitoshi daga hadisin Abu Huraira (Allah Ya kara masa yarda).
Kuma an sunnanta wa mumini yin wannan addu’ar domin ya hada tsakanin tsarkin ruhi da tsarkin jiki.
Nau’i na biyu: najasa ta hissi (wato wacce ake iya gani) itace duk wani abu da ake iya shaida samuwarsa wanda shari’a ta hukunta kasancewarsa najasa bisa kashin kansa ba bisa sifansa ta ma’anaba, kamar bawali, da haila, da kare, da alade, da mushe.
Najasa ta hissi ta kasu kashi biyu:
Kashi na farko:najasa ta asali, abun nufi da ita shine abubuwanda asalinsu najasoshine kamar abubuwanda aka buga misali dasu a baya.
Kashi na biyu: najasa ta hukunci, sune abubuwanda suke da tsarki (a asali) amma (haduwarsu da) najasoshi ya maida su najasa.
Misalin haka: tufafi sakakke da zarurruka masu tsarki; idan najasa ta fada akansa, to hukuncinsa shine najastuwa, idan aka gusarda najasar, sai ayi hukunci da cewa shi mai tsarkine.
Banbanci tsakanin najasa (ainiyya) da najasa (hukmiyya) shine: najasa (ainiyya) bazai yiwu a tsarkakeshi ba, saboda haka kare da za’a wanke shi saw dari bazai tsarkaka ba har abada.
Amma kwanon da kare yayi lallage acikinsa, to shi kwnon ya zama najastacce a hukunci, saboda haka idan aka wankeshi saw bakwai daya daga cikin (wankin) aka sanya kasa, sai ayi hukunci da cewa ya tsarkaka.
Banbanci tsakanin kazanta da najasa:
Daga cikin abinda ya kamata a sani shine, ba kowace dawdace najasaba, saboda haka abinda ke kasancewa ajikin tufafi na kura da zufa da jirkitan lawninsa sakamakon haka ko sakamakon an rinashi da wasu naw’uka na rini masu tsarki, to wannan bazai sashi ya zama najastacceba, a’a shi mai tsarkine koda kuwa bai kasance mai tsaftaba, kuma tsarkakuwa daga hadasi da gushewar khabasi dashine tsarki ke tabbata.
Hukuncin dahara:
Dahara tana wajaba, aduk sa’adda wani aiki ya halarto wanda ba’a yinsa sai da tsarki, mafi girma cikin wadannan (wato ayyukanda ba’ayinsu said a tsarki) itace salla.
Saboda haka idan salla ta halarto, to dahara ta wajaba akan wanda duk yake da hadasi, kuma bai halatta agareshi ya jinkirta salla daga lokacinta ba, hakananma ya wajaba ga mai janaba yayi wanka idan yana bukatan zama acikin masallaci, baya halatta agareshi ya zawna acikin masallaci alhali yana mai janaba, sai dai mai ketare hanya, kamar ya shigo ta wata kofa ya fice ta wata kofa saboda wata bukatarsa zuwa haka.
Wanda yakeda yalwan lokaci, yahalatta gareshi ya jinkirta dahara daga hadasi har zuwa lokacin wajibcinta (wato lokacin salla ko makamancin ta). Hakananma wanda yayi mafarki tun farkon yini, to ya halatta gareshi ya jinkirta wankansa –in yaso- har zuwa shigan lokacin sallar azahar.
Sharuddan wajibcin dahara:
Kuma tsarkakuwa daga hadasi wajibine ga duk wanda ke cikn hadasi (wato wanda keda janaba ko wanda baida alwala), baligi, mai hankali, wanda yakeda ikon tsarkaka, masani gameda wajibcin dahara da yadda ake daharar.
Amma wanda baya cikin hadasi, to ba wajibi bane sai ya maimaita dahara idan lokacin salla ya shigo matukar alwalarsa bata warwareba.
Wanda bai balagaba kuwa, tsarki daga hadasi bai wajaba akansaba, saboda hukunce hukuncen shari’a basu haw kansaba, idan ya girma ya kai mumayyizi (wato shekara bakwai) za’a karbi aikinsa in yayi kuma za’a bashi lada. Kuma anso ga masu kula dashi su tarbiyantar dashi akan yin salla da yin tsarki.
Amma mara hakali, wato mahawkaci da duk wanda hankalinsa ya gushe sakamakon wata illa, to dahara bata wajaba akansaba, har sai hankalinsa ya dawo jikinsa, saboda hankali sharadine na wajibcin hukunce hukuncen shari’a.
Wanda baida ikon yin dahara kuwa sakamakon wani rashin lafiya ko gajiyawa da makamantan haka, to za’a sassawta masa, idan yana iya yin taimama, sai yayi taimama, idan kuma baya iyawa sai yayi sallar a halin da yake, kuma za’ayi la’akari dashi amatsayin mai tsarki a hukunce.
Amma jahili wanda baida ilimi gameda wajibcin dahara, kamar wanda ya tashi a wani yankinda jahilci gameda hukunce hukuncen addini ya yawaita, ko kuma wanda ya musulunta bada jumawaba (saboda haka) baisan abubuwanda ke wajabta (samuwar) hadasiba da abinda ke gusar dashi, to lallai wannan za’ayi masa uzuri saboda jahilcinsa domin Allah baYa azabtar da wanda hujja bata tsayu akansaba, kamar yadda Allah (madawkakin Sarki) Yace:
{وما كنّا معذبين حتى نبعث رسولاً}
Ma’ana:”Kuma baMu kasance maSu yin azababa har sai Mun aika wani Manzo”
Kuma ya wajaba agareshi ya nemi ilimin addini gwargwadon iyawarsa, kuma wajibine akan wanda yasan halin da yake ciki daga cikin musulmai ya karantar dashi kuma ya shiryar dashi.
Kuma wannan – har wayaw- shine hukuncin wanda shi kuma ya san cewa dahara wajibace amma bai san yadda zaiyi alwalaba, hakanan baisan yadda zaiyi ingantacciyar wankaba, wannan yakan faru da wasu mutane idan ilimi yayi karanci (acikinsu) kuma jahilci yayadu.
Kuma ya kamata masanin fikihu ya san hukuncin irin wadannan (mutanen) ayayin da zai bukatu zuwaga yi musu fatawa da kuma karantarwa.
Sharuddan ingancin dahara:
Sharuddan ingancin dahara sune: musulunci, hankali, tamyizi (wato ya iya rarrabewa tsakanin abubuwa, wannan kuwa yakan farane daga shekara bakwai), niyya, gushewar abinda zai iya hana dahara tareda kudura (wato ikion gusarwan), zuwa da gwargwadon abindake wadatarwa na dahara, da shigan lokaci ga wanda yakeda hadasi na dindindin.
Amma shardanta musulunci, ya kasancene saboda dahara ibadace, ibada kuma bata inganta daga kafiri har saiya zama musulmi.
Hankali kuwa, saboda wanda baida hankali bubu niyya agareshi.
Tamyizi kuwa (wato hankalin da ya kai yaro ya iya rarrabewa tsakanin abubuwa an shrdantashine) saboda dan karamin yaronda bai kai matsayin rarrabewaba, niyyarsa bata inganta.
Niyya kuwa, saboda alwala aikine, aiki kuwa baya inganta saida niyya. Saboda fadin Annabi (tsira da amincin Allah su tabbata agareshi):
((إنما الأعمال بالنيات))
Ma’ana:”Babu aiki saida niyya”
Saboda haka ita (niyya) sharadice acikin alwala da wanak da taimama. Amma (abinda ya shafi) gusar da najasa, to (shikam) ba’a shardanta masa niyya, saboda shi yana cikin abubuwanda ake neman rabuwa da wofantuwa daga gare sune.
Niyya mahallinta shine zuciya, furtata kuwa bidi’ace.
Gushewar abinda zai hana tsarkakuwa kuwa, yanada misalai; daga cikinsu akwai haila da biki (wato jinin haihuwa) saboda haka daharar mace bazata ingantaba har sai ta tsarkaka daga hailarta ko bikinta, kuma duk wacce tayi dahara alhali tana cikin haila, to dahararta (wato alwala ko wankan tsarki) bai ingantaba.
Ana toge mai janaba (daga cikin wannan sharadin) idan yayi nufin yin bacci, to shi anso agareshi yayi alwala, saboda hadisi ingantacce daya zo akan haka, sai dai bazai yi salla da wannan alwalarba har sai yayi wanka.
Hakananma wanda ya sanya wani abu wanda zai hana isan ruwa zuwa ga fata a gurabun alwala, to ya wajaba agareshi ya gusardashi, saidai wanda akayi rangwame agamedasu, kamar huffi, da bandeji da irin filastocin da ake likawa akan rawnunnuka da makamantasu.
Amma zuwada gwargwadon abinda ke wadatarwa na dahara, bayanisa zaizo adarasi na gaba in Allah (Madawkakin Sarki Ya yarda).
Shigan lokaci kuwa sharadine na inganci ga wanda yakeda hadasi na dindindin, kamar (mace) mai jinin istihada (wato jinin cuta) da wanda keda yoyon fitsari da makamantansu, wadannan su zasu rika yin alwala ga kowace salla sannan sai suyi sallarsu (da alwalar) koda kuwa hadasin ya cigaba da fitowa wato bai tsayaba bayan alwala kamar yadda bayaninsa zaizo acikin darussa na gaba in Allah (Madawkakin Sarki Ya yarda).

Abinda tsarki ke kasancewa dashi:
Khulasar abinda bayaninsa ya gabata shine: lallai dahara daga khabasi yana kasancewne ta hanyar gusardashi ayayin da aka samu ikon hakan, kuma cewa dahara daga babban hadasi yana kasancewane da wanka, dahara daga karamin hadasi kuma yana kasancewane da alwala. Duk wanda bai samu ruwaba ko kuma ya gaza yin anfani dashi sai yayi taimama, idan kuma ya gaza yinsu duka biyu, sai yayi salla ahalinda ya samu kansa sai hukuncinsa ya kasance na mai tsarki.
Abubuwanda ba’ayinsu saida alwala:
Malamai sunyi ijma’i akan cewa tsarki daga naw’uka biyu na hadasi (wato babba da karami) sharadine gameda ingancin salla, amma sunyi sabani gameda taba Alkur’ani da dawafi gamai karamin hadasi.
Bayanin wadannan mas’alolin zaizo a gurbinsa in Allah Ya yarda, kawai makasudin wannan darasin shine, sanin (bayanin) gamammun hukunce hukunce gameda tsarki. Kuma Allah Shine Mai datarwa kuma Mai shiryarwa zuwaga tafarki madaidaici.