تسجيل الدخول

مشاهدة النسخة كاملة : الدرس السادس: بَيانُ معنَى العِبادةِ


عبد الله الداخل
_21 _March _2013هـ الموافق 21-03-2013م, 11:24 PM
الدرس السادس: بَيانُ معنَى العِبادةِ
العِبادةُ هي: التَّذلُّلُ والخُضوعُ والانقيادُ مع شدَّةِ المحبَّةِ والتعظيمِ.
وكلُّ عَمَلٍ يُتقرَّبُ به إلى المَعْبودِ فهو عِبادةٌ.
ولذلك فإنَّ العبادةَ الشَّرْعِيَّةَ هي اسمٌ جامعٌ لكلِّ ما يُحبُّه اللهُ ويَرْضاهُ من الأقوالِ والأعمالِ الظاهرةِ والباطنةِ.
والعبادةُ تكونُ بالقلبِ واللسانِ والجوارحِ، وقد أمَرَ اللهُ تعالى بإخلاصِ العبادةِ له وَحْدَه لا شَريكَ له؛ قال اللهُ تعالى: ﴿هُوَ الْحَيُّ لَا إِلَهَ إِلَّا هُوَ فَادْعُوهُ مُخْلِصِينَ لَهُ الدِّينَ الْحَمْدُ لِلَّهِ رَبِّ الْعَالَمِينَ (65)﴾ [غافر: 65].
وقال تعالى: ﴿قُلْ إِنِّي أُمِرْتُ أَنْ أَعْبُدَ اللَّهَ مُخْلِصًا لَهُ الدِّينَ﴾ [الزمر: 11].
وأمَرَ اللهُ باتِّباعِ رسولِه صلى الله عليه وسلم وأداءِ العبادةِ على الهَدْيِ الذي بَيَّنَهُ لنا، قال اللهُ تعالى: ﴿وَأَنْزَلْنَا إِلَيْكَ الذِّكْرَ لِتُبَيِّنَ لِلنَّاسِ مَا نُزِّلَ إِلَيْهِمْ﴾[النحل: 44]، وقال: ﴿وَمَا آتَاكُمُ الرَّسُولُ فَخُذُوهُ وَمَا نَهَاكُمْ عَنْهُ فَانْتَهُوا﴾ [الحشر: 7]
واللهُ تعالى لا يَقْبَلُ عبادةً من أحدٍ إلا بتَحْقيقِ هَذَينِ الشَّرْطينِ: الإخلاصِ والمُتابعةِ.
والعبدُ لا يكونُ مسلمًا حتى يُخْلِصَ الدِّينَ للهِ تعالى، ويَتَّبِعَ الرسولَ صلى اللهُ عليه وسلم.
فمَن أدَّى العبادةَ خالصةً للهِ تعالى، وصَوابًا على سُنَّةِ رسولِ اللهِ صلى اللهُ عليه وسلم فهي عبادةٌ صحيحةٌ، وعَمَلٌ صالِحٌ.

وقد بَيَّن اللهُ تعالى لنا في كتابِه الكريمِ أنه خَلَقَنا لغَايةٍ عظيمةٍ، وهي عبادتُه وحدَه لا شَرِيكَ له، قال اللهُ تعالى: ﴿وَمَا خَلَقْتُ الْجِنَّ وَالْإِنْسَ إِلَّا لِيَعْبُدُونِ﴾ [الذاريات: 56].
وقال تعالى: ﴿وَمَا أُمِرُوا إِلَّا لِيَعْبُدُوا اللَّهَ مُخْلِصِينَ لَهُ الدِّينَ حُنَفَاءَ وَيُقِيمُوا الصَّلَاةَ وَيُؤْتُوا الزَّكَاةَ وَذَلِكَ دِينُ الْقَيِّمَةِ﴾ [البينة: 5].
* فمَن اجْتَنَبَ الشِّرْكَ وأخْلَصَ العِبادةَ للهِ تعالى واتَّبَعَ الرَّسولَ فهو مُسلمٌ مَوعودٌ بدُخولِ الجَنَّةِ والنَّجاةِ من النارِ.
* ومَن أدَّى العباداتِ الواجبةَ؛ فامتثَلَ ما أوْجَبَه اللهُ، واجتَنَبَ ما حَرَّمَه اللهُ؛ فهو من عِبادِ اللهِ المُتَّقينَ المُؤمِنينَ الذين كتَبَ اللهُ لهم الأمنَ من العذابِ، ووَعَدَهم الفَضْلَ العظيمَ في الدنيا والآخرةِ.
* ومَن كمَّل العباداتِ الواجبةَ والمُستحبَّةَ واجتنَبَ المُحرَّماتِ والمَكْروهاتِ؛ فعَبَدَ اللهَ كأنَّه يَرَاهُ؛ فهو من عِبَادِ اللهِ المُحْسِنينَ الذين وعَدَهم اللهُ الدَّرَجاتِ العُلَى من الجَنَّةِ.

وبهذا تَعْلَمُ أن ما يَقْدَحُ في عُبودِيَّةِ العبدِ لرَبِّه عز وجل على ثَلاثِ دَرَجاتٍ:
الأُولَى: الشِّرْكُ الأكبرُ، وهو عِبادةُ غيرِ اللهِ عز وجل؛ فمَن صَرَفَ عبادةً من العباداتِ لغَيْرِ اللهِ عز وجل؛ فهو مُشرِكٌ كافرٌ، لا يَقْبَلُ اللهُ منه صَرْفًا ولا عَدْلاً، كالذين يَدْعُونَ الأصنامَ والأولياءَ والأشجارَ والأَحْجَارَ، ويَذْبَحُونَ لها ويَسْألُونَها قَضاءَ الحَوائجِ ودَفْعَ البَلاءِ.
وهؤلاء كُفَّارٌ مُشرِكونَ خارجونَ عن دينِ الإسلامِ، مَن ماتَ منهم ولم يَتُبْ فهو خَالِدٌ مُخلَّدٌ في نارِ جَهَنَّم والعياذُ باللهِ.

الدرجةُ الثانيةُ: الشِّرْكُ الأَصْغَرُ، ومنه الرِّياءُ والسُّمْعةُ، فيُزَيِّنُ العبدُ عبادتَه من صلاةٍ وصدقةٍ وغيرِها لأجلِ أنْ يَمْدَحَهُ الناسُ بذلك، فمَن فعَلَ ذلك فهو غيرُ مُخْلِصٍ للهِ تعالى الإخلاصَ الذي يَنْجُو به من العذابِ، فهو وإنْ لم يَعْبُدْ غيرَ اللهِ حقيقةً إلا أنه بطَلَبِه ثَناءَ الناسِ ومَدْحَهم وإعجابَهم قد ابْتَغَى ثَوابَ العِبادةِ من غيرِ اللهِ عز وجل، وهو مُشرِكٌ شِرْكًا أصْغَرَ يُحْبِطُ تلك العبادةَ، وقد قال النبيُّ صلى اللهُ عليه وسلم فيما يَرْويِه عن رَبِّه جل وعلا أنه قالَ: [أنَا أَغْنَى الشُّرَكَاءِ عن الشِّرْكِ، مَن عَمِلَ عَمَلاً أشْرَكَ معي فيه غيري تَرَكْتُه وشِرْكَه] رواه مسلمٌ من حديثِ أبي هُريرةَ رضِي الله عنه.
ومن الشِّرْكِ الأَصْغَرِ أن يَتعَلَّقَ قَلْبُ العَبْدِ بالدنيا حتى تكونَ أكْبَرَ هَمِّه ويُضَيِّعَ بسَبَبِها الواجباتِ ويَرْتَكِبَ المُحرَّماتِ؛ فيَكونَ في قَلْبِه عُبودِيَّةٌ للدنيا، وقد قال النبيُّ صلى اللهُ عليه وسلم: ((تعِسَ عَبدُ الدِّينارِ وعَبْدُ الدِّرْهمِ وعبدُ الخَمِيصةِ إنْ أُعْطِيَ رَضِيَ وإنْ لم يُعْطَ سَخِطَ، تَعِسَ وانتكَسَ وإذا شِيكَ فلا انْتَقَشَ)). رواه البخاريُّ من حديثِ أبي هُريرةَ رضِي اللهُ عنه.
وهذا دعاءٌ عليه من النبيِّ صلى الله عليه وسلم بالتَّعاسةِ والانتكاسةِ، فكُلَّما قامَ من سَقْطةٍ وقَعَ في أُخْرَى، وإذا أُصِيبَ ببلاءٍ لم يَهْتَدِ للخُروجِ منه، وسببُ ذلك عُبودِيَّتُه للدُّنيا، وغَفْلتُه عن اللهِ جل وعلا.
وقد بَيَّن النبيُّ صلى الله عليه وسلم الضابطَ في ذلكَ فقالَ: ((إنْ أُعْطِيَ منها رَضِيَ وإن لم يُعْطَ سَخِطَ)).
فإذا كانَت همَّةُ العبدِ للدُّنيا إنْ أُعْطِيَ منها رضِيَ، وإن لم يُعْطَ ظَلَّ ساخِطًا على قَضاءِ اللهِ وقَدَرِه مُتَبَرِّمًا منه لم يَكُنْ قَلْبُه سليمًا للهِ جل وعلا، وهذا من شأنِ المُنافِقِينَ، كما قال اللهُ تعالى فيهم: ﴿وَمِنْهُمْ مَنْ يَلْمِزُكَ فِي الصَّدَقَاتِ فَإِنْ أُعْطُوا مِنْهَا رَضُوا وَإِنْ لَمْ يُعْطَوْا مِنْهَا إِذَا هُمْ يَسْخَطُونَ﴾ [التوبة: 58]، فرِضَاهُم لغَيْرِ اللهِ وسَخَطُهم لغيرِ اللهِ.

ومَن كان هذا حالَهُ فهو غير مخلصٍ العبادَةَ للهِ تَعَالَى، بل في قلبه عُبودِيَّةٌ لغيرِ اللهِ جَلَّ وَعَلا، وهذا أمرٌ تُشاهَدُ آثارُه فيمَن تعلَّقَ قلبُه بمالٍ أو رئاسةٍ أو شَخْصٍ يُحِبُّه حتى يَعْصِيَ اللهَ لأجلِه؛ فيكونَ في قَلبِه رِقٌّ لما أحبَّه وتَعلَّقَ به وعَصَى اللهَ لأجله، ومَن تعلَّق شيئًا دونَ اللهِ عُذِّبَ به.

الدرجةُ الثالثةُ: فِعْلُ المعاصي، وذلك بارتكابِ بعضِ المُحرَّماتِ أو التفريطِ في بعضِ الواجباتِ، وكلما عَصَى العبدُ رَبَّه كان ذلك نَقْصًا في تَحْقيقِه العبوديةَ للهِ تعالى.
وأكملُ العبادِ عُبوديَّةً للهِ تعالى أحسنُهم استقامةً على أمرِ اللهِ عز وجل، قال اللهُ تعالى: ﴿إِنَّ الَّذِينَ قَالُوا رَبُّنَا اللَّهُ ثُمَّ اسْتَقَامُوا فَلَا خَوْفٌ عَلَيْهِمْ وَلَا هُمْ يَحْزَنُونَ (13) أُولَئِكَ أَصْحَابُ الْجَنَّةِ خَالِدِينَ فِيهَا جَزَاءً بِمَا كَانُوا يَعْمَلُونَ (14)﴾ [الأحقاف: 13–14].
وقال تعالى: ﴿إِنَّ الَّذِينَ قَالُوا رَبُّنَا اللَّهُ ثُمَّ اسْتَقَامُوا تَتَنَزَّلُ عَلَيْهِمُ الْمَلَائِكَةُ أَلَّا تَخَافُوا وَلَا تَحْزَنُوا وَأَبْشِرُوا بِالْجَنَّةِ الَّتِي كُنْتُمْ تُوعَدُونَ (30) نَحْنُ أَوْلِيَاؤُكُمْ فِي الْحَيَاةِ الدُّنْيَا وَفِي الْآَخِرَةِ وَلَكُمْ فِيهَا مَا تَشْتَهِي أَنْفُسُكُمْ وَلَكُمْ فِيهَا مَا تَدَّعُونَ (31) نُزُلًا مِنْ غَفُورٍ رَحِيمٍ (32) وَمَنْ أَحْسَنُ قَوْلًا مِمَّنْ دَعَا إِلَى اللَّهِ وَعَمِلَ صَالِحًا وَقَالَ إِنَّنِي مِنَ الْمُسْلِمِينَ (33)﴾ [فصلت: 30–33].

ومدارُ عُبودِيَّةِ القَلْبِ على ثلاثةِ أمورٍ عظيمةٍ هي: المَحَبَّةُ، والخَوْفُ، والرَّجاءُ.
ويَجِبُ على العَبْدِ أن يُخْلِصَ هذه العباداتِ العظيمةَ للهِ تعالى:
– فيُحِبَّ اللهَ تعالى أعظمَ مَحَبَّةٍ، ولا يُشْرِكَ معه في هذه المَحبَّةِ العظيمةِ أحدًا من خلقِه، كما قال اللهُ تعالى: ﴿وَالَّذِينَ آَمَنُوا أَشَدُّ حُبًّا لِلَّهِ﴾ [البقرة: 165].
– ويَخافَ من سَخَطِ اللهِ وعِقابِه، حتى يَنْزجِرَ عن فعلِ المعاصي من خَشْيةِ اللهِ تعالى.
– ويَرْجوَ رحمةَ اللهِ ومَغْفرتَه وفَضْلَهُ وإحسانَهُ.
ومَن كان كذلكَ فإنه لا يَيْأسُ من رَوْحِ اللهِ، ولا يَأْمَنُ مَكْرَ اللهِ، بل يَبْقَى جامِعًا بينَ الرَّجاءِ والخَوفِ كما أمَرَ اللهُ تعالى عبادَه بقولِه: ﴿وَادْعُوهُ خَوْفًا وَطَمَعًا إِنَّ رَحْمَتَ اللَّهِ قَرِيبٌ مِنَ الْمُحْسِنِينَ﴾ [الأعراف: 56].
فالدُّعاءُ هنا يَشْمَلُ دُعاءَ المَسْألةِ ودُعاءَ العِبادةِ.

● ومَحبَّةُ العبدِ لربِّه تعالى تَدْفَعُه إلى التقرُّبِ إليه، والشَّوقِ إلى لقائِه، والأُنسِ بذِكْرِه، وتَحْمِلُه على مَحَبَّةِ ما يُحِبُّه اللهُ، وبُغْضِ ما يُبْغِضُه اللهُ، فيُحَقِّقُ عُبوديَّةَ الولاءِ والبَرَاءِ بسببِ صِدْقِ مَحبَّتِه للهِ تعالى.
● وخَوفُه من اللهِ يَزْجُرُه عن ارتكابِ المُحرَّماتِ وتركِ الواجباتِ؛ فيكونُ من عبادِ اللهِ المُتَّقينَ، الذين حَمَلَتْهم خَشْيةُ اللهِ تعالى على اجتنابِ أسبابِ سَخَطِه وعِقابِه.
● ورَجاؤُه للهِ يَحْفِزُه على فِعْلِ الطاعاتِ لما يَرْجُو من عَظيمِ ثَوابِها وبَرَكةِ رِضْوانِ اللهِ عز وجل على أهلِ طَاعَتِه.

طاهر جبريل دكو
_2 _April _2013هـ الموافق 2-04-2013م, 07:28 AM
Darasi na shida: Bayani gameda ma'anar ibada.
Ma'anar Kalmar ibada a harshen larabci shine, Kankan da kai da tawalu'u da jawuwa (wato bin umurnin Allah sau da kafa).
Kuma dukkanin aikin da za'ayi domin neman kusanci ga abin bawta, to shine ibada.
Saboda haka ibada a mahanga ta shari'a sunace gamammiya da ta kunshi dukkanin abinda Allah Yakeso kuma Ya yarda dashi daga maganganu da ayyuka na sarari dana boye.
Kuma ibada takan kasance da zuciya da harshe da gabbai, hakika Allah (madawkaki) Yayi umurni da tsarkake bawta gareShi Shikadai batareda sanya maSa abokin tarayya ba. Allah(madawkaki) Yace:
﴿هُوَ الْحَيُّ لَا إِلَهَ إِلَّا هُوَ فَادْعُوهُ مُخْلِصِينَ لَهُ الدِّينَ الْحَمْدُ لِلَّهِ رَبِّ الْعَالَمِينَ (65)﴾ [غافر: ٦٥].
Ma'ana:" Shine Rayayye babu wni abin bawtawa da gaskiya sai Shi, ku kirayeShi alhali kuna masu tsarkake Addini gareShi. Godiya ta tabbata ga Allah Ubangijin talikai.
Q40: ayata65. Kuma (Madawkaki sarki) Yace:

﴿قُلْ إِنِّي أُمِرْتُ أَنْ أَعْبُدَ اللَّهَ مُخْلِصًا لَهُ الدِّينَ﴾ [الزمر: ١١].
Ma'ana:" Kace (musu ya Muhammad) "Lallai ni an umurceni da in bawtawa Allah alhali in mai tsarkake bawta gareShi" Q39: ayata11.
Kuma Allah Yayi umurni da bin bayyana ManzonSa (S.A.W) da aywatar da bawta akan shiriyarsa wacce ya garemu. Allah (Madawkakin Sarki) Yace:
﴿وَأَنْزَلْنَا إِلَيْكَ الذِّكْرَ لِتُبَيِّنَ لِلنَّاسِ مَا نُزِّلَ إِلَيْهِمْ﴾[النحل: ٤٤]،
Ma'ana:" Kuma Mun sawkar maka da Ambato (wato Alkur'ni) domin kabayyana wa mutane abinda akasawkar zuwa garesu.Q16: ayata44. Kuma Yace:
وقال: ﴿وَمَا آتَاكُمُ الرَّسُولُ فَخُذُوهُ وَمَا نَهَاكُمْ عَنْهُ فَانْتَهُوا﴾ [الحشر: ٧]
Ma'ana:"Duk abinda Manzon(Allah ) yazo muku dashi to ku karba, kuma duk abind ya haneku, to ku hanu" Q59: ayata7.
Kuma Shi Allah baYa karban wata ibada daga wurin wani har sai ta cika wadannan sharudda guda biyu; Iklasi (wato yi domin Allah), da koyi da Manzon Allah (.S.A.W))
Bawa bazai zama Musulmi ba har sai ya tsarkake addininsa ga Allah (Madawkakin Sarki) kuma yayi koyi da Manzon Allah (S.A.W)
Saboda haka duk wanda yayi ibada bias ikhlasi ga Allah (Madawkakin Sarki) kuma daidai bias koyarwan Manzon Allah (S.A.W) to wannar itace bawta ingantacciya kuma shine aiki mai kyaw.
Kuma hakika Allah (Madawkakin Sarki) acikin littafinSa mai karimci Ya bayyana mana cewa lallai Ya haliccemu ne don wata manufa mai girma wacce itace bawtanSa Shi kadai batareda sanya maSa abokin tarayya ba Allah (Madawkakin Sarki) Yace:
﴿وَمَا خَلَقْتُ الْجِنَّ وَالْإِنْسَ إِلَّا لِيَعْبُدُونِ﴾ [الذاريات: ٥٦].
Ma'ana:"Kuma ban halicci Aljani da Mutun ba face don su bawta miNi. Q51: ayata56. Kuma Allah(Madawkakin Sarki) Yace:

﴿وَمَا أُمِرُوا إِلَّا لِيَعْبُدُوا اللَّهَ مُخْلِصِينَ لَهُ الدِّينَ حُنَفَاءَ وَيُقِيمُوا الصَّلَاةَ وَيُؤْتُوا الزَّكَاةَ وَذَلِكَ دِينُ الْقَيِّمَةِ﴾ [البينة: ٥].

Ma'ana:"Kuma ba'a umurcesu da komaiba face dasu bawtawa Allah, suna masu tsarkake addini gareShi, masu karkata zuwaga Addinin gaskiya, kuma su tsaida sallah kuma su bayarda zakka, kuma wannan shine Addinin (mabiya tafarkin) kwarai. Q98ayata5.
Saboda haka wanda ya nisanci shirka ya kuma tasrkake ibada ga Allah (Madawkakin Sarki) kuma ya bi Manzon Allah (S.A.W) to shine Musulmi wanda akayiwa alkawarin shiga Aljanna da kubuta daga (shiga) Wuta.
Duk wanda ya aiwatar da bawta na wajibi, wato ya bi umurni cikin abinda Allah Ya wajabta, ya kuma nisanci abinda Allah Ya haramta, to (wannan) yana cikin bayin Allah masu takawa muminai, wadanda Allah Ya rubuta musu aminci daga azaba, kuma Yayi musu alkawarin falala mai girma anan Duniya da ranan karshe.
Duk kuma wanda ya kamala (ayyukan) ibada na wajibi da na mustahabbi ya kuma nisanci abubuwanda aka haramta da wadanda aka karhanta, wato ya bawtawa Allah tamkar yana ganinSa, to (wannan) yana cikin bayin Allah muhsinai wadanda Allah Yayiwa alkawarin darajoji madawkaka agidan Aljanna.

Kuma da wannanne zaka fahimci cewa abinda ke lalata cikin bawtar bawa ga ubangijinsa (Mai girma da dawkaka) (abubuwane dake bisa) darajoji guda uku
Daraja ta farko:Babbar shirka, itace bawtan wanin Allah (Mai girma da dawkaka). Duk wanda ya aiwatarda wani naw'i na bawta ga wanin Allah (Mai girma da dawkaka) to shi mushurikine, kafiri. Allah bazai karbi ayyukan farilla ba hakama ta nafila daga gareshi. Kamar wadanda suke bawtar gumaka da waliyyai da bishiyoyi da duwatsu. Kuma suke yin yanka dominsu kuma suke rokonsu biyan bukatu da tunkude bala'o’i.
To wadannan kafiraine mushurikai, wadanda suka yi ridda daga addinin Musulunci. Duk wanda ya mutu a cikinsu batare daya tubaba, zai dawwama acikin Wutar Jahannama, Allah Ya tsaremu

Daraja ta biyu: Karamar shirka, daga cikin (misalanta akwai) riya, da sum'a (wato yin aiki domin nuna bajinta ko neman yabo) sai bawa ya kyawtata aikinsa na bawta sallah da sadaka da waninsu domin mutane su yabeshi akai. Duk wanda ya aikata haka to shi ba mai ikhlasi bane ga Allah cikin ibada irin ikhilasinda ke tseratarwa daga azaba. Shi (wannan) duk da cewa bai bawtawa wanin Allah ba bisa hakika, saidai kasancewarsa ya nemi yabo da bajinta da burgewa daga mutane, to ya nemi ladane daga wurin wanin Allah (Mai girma da dawkaka) (da wannan) shi mushirikine karamar shirka wacce ta rusa wannan ibadar (da akayi tada wannan manufar). Hakika Annabi (S.A.W) ya fadi cikin abinda yaruwaito daga Ubangijinsa (Mai girma da dawkaka) cewa lallai Yace:
: [أنَا أَغْنَى الشُّرَكَاءِ عن الشِّرْكِ، مَن عَمِلَ عَمَلاً أشْرَكَ معي فيه غيري تَرَكْتُه وشِرْكَه] رواه مسلمٌ من حديثِ أبي هُريرةَ رضِي الله عنه.
Ma'ana:"Nine mafi wadatuwa - cikin wadanda akeyiwa tarayya- daga abokin tarayya, duk wanda yayi wani aiki ya hadaNi da waniNa acikinsa, to Na barshi da shirkansa" Musulim ne ya ruwaito shi daga hadisin Abu huraira (Allah Ya kara masa yarda).
Kuma yana daga cikin karamar shirka zuciyar bawa ta ta'allaka da Duniya har Duniya ta zama itace mafi girman damuwarsa don haka sai yayi wasa da wajibai asanadinta ya kuma aikata ayyukan haramun, saboda haka sai bawtar Duniya ta kasance acikin zuciyarsa. Hakika Annabi (S.A.W) yace:
((تعِسَ عَبدُ الدِّينارِ وعَبْدُ الدِّرْهمِ وعبدُ الخَمِيصةِ إنْ أُعْطِيَ رَضِيَ وإنْ لم يُعْطَ سَخِطَ، تَعِسَ وانتكَسَ وإذا شِيكَ فلا انْتَقَشَ)). رواه البخاريُّ من حديثِ أبي هُريرةَ رضِي اللهُ عنه.
Ma'ana:"Bawan Duniya ya tabe, bawan dirhami (wato kudi) ya tabe, bawan sutura ya tabe, idan aka bashi sai ya yarda, inko ba'a bashiba sai ya yi fushi, ya tabe kuma ya rigingina kuma idan ya taka kaya kada ya samu ikon cirewa" Bukharine ya ruwaitoshi daga hadisin Abu huraira (Allah Ya kara masa yarda).
Wannan addu'ace Annabi (S.A.W) yakeyi akansa da tabewa da (tafiya a) rigingine duk sa'adda ya tashi daga wata faduwa sai ya sake komawa wata, kuma iadan wata masifa ta sameshi bai iya sanin mafita daga cikinta. Kuma sababibn wannan shine bawtan Duniya da gafala daga Allah (Mai girma da dawkaka).
Annabi (S.A.W) ya riga ya bayyana ka'idar gane haka inda yace:
((إِذَا أُعْطِيَ منها رَضِيَ وإن لم يُعْطَ سَخِطَ)).
Ma'ana:"Idan aka bashi sai ya yarda, idan kuma ba'a bashi ba, sai yayi fushi.

Idan burin bawa ya kasance shine Duniya in aka bashi ya yarda inkuma aka hanashi ya doge cikin fushi gameda hukuncin Allah da kaddaransa yana mai kwarmato gameda shi, zuciyarsa bata kasance amintacciyaba ga Allah (Madawkakin Sarki) wannan shine sha'anin munafukai. Kamar yadda Allah Ya fadi gamedasu:
﴿وَمِنْهُمْ مَنْ يَلْمِزُكَ فِي الصَّدَقَاتِ فَإِنْ أُعْطُوا مِنْهَا رَضُوا وَإِنْ لَمْ يُعْطَوْا مِنْهَا إِذَا هُمْ يَسْخَطُونَ﴾ [التوبة: ٥٨]، فرِضَاهُم لغَيْرِ اللهِ وسَخَطُهم لغيرِ اللهِ.
Kuma daga cikinsu akwai wanda yake zundenka a sha'anin sadaka, idan anbasu daga cikinta sai su yarda, idan kuma ba'a basu daga cikinta ba sai su dawra yin fushi." Q9: ayata58. Wato su yardansu don wanin Allah sukeyi fushinsuma don wanin Allah ne.

Duk wanda halinsa ya kasance haka to shi ba mai tsarkake bawta ga Allah (Madawkakin Sarki) bane, a'a acikin zuciyarsa akwai bawtuwa ga wanin Allah (Mai girma da dawkaka), wannan ana iya ganin tasirinsa daga wanda zuciyarsa ta ta'allaka ga dukiya, ko shugabanci, ko wani wanda yake kawna har sai ya kaiga sabawa Allah a sanadinsa, saboda haka sai a samu bawta a cikin zuciyarsa ga wannan abin da yake kawna kuma zuciyarsa ta ta'allaka dashi sai kaga harma yana iya sabawa Allah a sansdinsa, duk wanda ya rataya zuciyarsa da wani abu koma bayan Allah (Madawkakin Sarki) sai an azabtaddashi dawannan abun.
Daraja ta uku: Aikata sabo, wannan yana nufin aikata wasu haramtattun abubuwa ko kuma sakaci cikin wasu wajibai. Duk as'adda bawa ya sabawa ubangijinsa wannan zai zama tawaya acikin bawtarsa ga Allah (Madawkakin Sarki).
Mafi kamala cikin bayi gameda bawta ga Allah (Madawkakin Sarki), shine wanda yafi tabbata akan umurnin Allah (Mai girma da dawkaka). Allah (Madawkakin Sarki) Yace:
﴿إِنَّ الَّذِينَ قَالُوا رَبُّنَا اللَّهُ ثُمَّ اسْتَقَامُوا فَلَا خَوْفٌ عَلَيْهِمْ وَلَا هُمْ يَحْزَنُونَ (13) أُولَئِكَ أَصْحَابُ الْجَنَّةِ خَالِدِينَ فِيهَا جَزَاءً بِمَا كَانُوا يَعْمَلُونَ (14)﴾ [الأحقاف: ١٣–١٤].
Ma'ana:" Lallaine wadanda sukace Allah Shine Ubangijinmu sannan kuma suka doge (akan haka) to (wadannan) basu da wani tsoro kuma bazasuyi bakin cikiba (13).
Wadannan ma'abuta Aljannane suna masu dawwama acikinta sakamako gameda abinda suka kasance suna aikatawa(14). Q46 ayata13da14. Kuma Allah (Madawkakin Sarki) Yace:
﴿إِنَّ الَّذِينَ قَالُوا رَبُّنَا اللَّهُ ثُمَّ اسْتَقَامُوا تَتَنَزَّلُ عَلَيْهِمُ الْمَلَائِكَةُ أَلَّا تَخَافُوا وَلَا تَحْزَنُوا وَأَبْشِرُوا بِالْجَنَّةِ الَّتِي كُنْتُمْ تُوعَدُونَ (30) نَحْنُ أَوْلِيَاؤُكُمْ فِي الْحَيَاةِ الدُّنْيَا وَفِي الْآَخِرَةِ وَلَكُمْ فِيهَا مَا تَشْتَهِي أَنْفُسُكُمْ وَلَكُمْ فِيهَا مَا تَدَّعُونَ (31) نُزُلًا مِنْ غَفُورٍ رَحِيمٍ (32) وَمَنْ أَحْسَنُ قَوْلًا مِمَّنْ دَعَا إِلَى اللَّهِ وَعَمِلَ صَالِحًا وَقَالَ إِنَّنِي مِنَ الْمُسْلِمِينَ (33)﴾ [فصلت: ٣٠–٣٣].
Ma’ana:”Lallaine wadanda sukace Ubangijinmu Shine Allah kuma suka doge akan haka, mala'iku na sassawka akansu (ayayin cikan ajalinsu) sunace musu kada kuji tsoro kuma kada kuyi bakin ciki, kuma kuyi bushara da Aljannar da kuka kasance ana muku alkawarinta (30) Mune majibintanku a rayuwar duniya da lahira, kuma kuna da duk abinda rayukanku ke shi'awa kuma kunada duk abinda kuka bukata (da akawo) muku(31) Wata liyaface daga Mai gafara Mai jinkai (32) Kuma wanene mafi kyaw ga Magana fiyeda wanda yayi kira zuwaga Allah kuma yace lallai ni Musulmine (33). Q41ayata30-33.
Bawtar zuci ta ginune akan abubuwa uku masu girma, sune: soyayya, tsoro da kuma fatan samun rahama.
Kuma ya wajaba ga bawa ya tasrkake niyya kan wadannan manya manyan ayyukan bawtan ga Allah (Madawkakin Sarki)
Saboda haka sai yaso Allah (Madawkakin Sarki) da soyayya mafi girma, kuma kada yayi maSa tarayya da wani daga halittunSa acikin wannan soyayyar mai girma, kamar yadda Allah (Madawkakin Sarki) Yace:
﴿وَالَّذِينَ آَمَنُوا أَشَدُّ حُبًّا لِلَّهِ﴾ [البقرة: ١٦٥].
Ma'ana:"Wadanda sukayi imani sune mafiya tsananin soyayya ga Allah. Q2:ayata165.
Kuma yaji tsoron fushin Allah da ukubarSa domin ya fadaka daga aikata sabo saboda tsoronsa ga Allah (Madawkakin Sarki).
Kuma yayi fatan samun Rahamar Allah da gafararSa da FalalarSa da kyawtatawarSa.
Duk wanda ya kasance hakannan to lallai kada ya fidda tsammani daga Rahamar Allah kuma kada ya aminta daga makircin Allah, a'a shidai zai tabbatane yana mai hadawa atsakanin tsammanin Rahama da tsoron azaba kamar yadda Allah (Madawkakin Sarki) Yayi umurni ga bayinSa cikin fadinSa:
﴿وَادْعُوهُ خَوْفًا وَطَمَعًا إِنَّ رَحْمَتَ اللَّهِ قَرِيبٌ مِنَ الْمُحْسِنِينَ﴾ [الأعراف: ٥٦].
Ma'ana:" Kuma ku kirayeShi kuna masu tsoron (azabarSa) kuma masu fatan (RahamarSa), lallai rahamar Allah kusa take ga masu kyawtatawa. Q7ayata56.
Saboda haka addu’a anan ta kunshi addu’a ta neman biyan bukata da addu’a ta (tsantsar) ibada.
Soyayyar bawa ga UbangijinSa (Madawkakin Sarki) tana tunkudashi izuwa ga kusantarSa da kuma kawnar saduwa daShi da samun nutsuwa ta hanyar ambatonSa, saboda haka sai ta sanyashi yarika son abinda Allah Yake so da kin abinda Allah Yakeki, da haka sai ya hakikance bawta ta bangaren wala'i da bara’i (kawnar mai kawnar Allah da kyamar makiyin Allah) saboda gaskiyarsa cikin soyayyaga Allah (Madawkakin Sarki).
Tsoronsa ga Allah kuma zai hanashi aikata ayyukan haram da barin wajibai, sai ya kasance daga cikin bayin Allah masu takawa wadanda tsoron Allah (Madawkakin Sarki) ya sa su suka nisanci abubuwanda ke sabbaba fushinSa (wato Allah) da ukubarSa.
Fatan samun Rahamar Allah kuma zai karfafa masa gwiwa wurin aikata ayyukan kwarai saboda abinda yake tsammanin samu na sakamako mai girma da albarka da yardan Allah (Mai girma da dawkaka) ga masu yimaSa da'a.